Alhaji Mamman Shata, waƙar 'Yarinya Lami Shagamu'

TSOKACI KAN WAƘAR 'YARINYA LAMI SHAGAMU' TA ALHAJI MAMMAN SHATA KATSINA A hirar da na taɓa yi da Hajiya Sadiya Adamu (Lami) a gidan ta a Kano, ta faɗa mani cewa ita 'yar asalin wani ƙauye mai suna Rigafada da ke Ƙaramar Hukumar Kumbotso a Jihar Kano ce. Yanzu ƙauyen ya bunƙasa, ya zama gari, ya ma haɗe da Kano; yana nan kudu da titin bypass ɗin nan da ya nufi yamma daga gadar nan ta farko idan za ka shiga Kano daga Zariya, wato wanda ya nufi Kabuga. Ba a daɗe da yaye ta ba yayar mahaifin ta ta zo ta ɗauke ta ta tafi da ita Legas domin ta riƙa ta. A can ta girma a unguwar Agege har ta fara ƙirgar dangi ba a taɓa zuwa Arewa da ita ba. Tana da shekara 11 sai gwaggon ta ta aurar da ita ga wani mutum. To amma saboda ba ta son mutumin, sai ta ƙi zama. Ta zauna a gida, yayin da mijin ya shigar da ƙara a kan lallai sai ta koma ɗakin sa. Bayan shekaru uku, a ranar 1 ga Oktoba, 1979, aka kashe auren. Daga nan sai ta zo Arewa ganin gida. Ta zauna a hannun kakar ta a Kano. A nan ta fara yawace-yawace. Zaman ba daɗi, sai ta ji gara ma zaman Legas. Don haka ta koma Legas. Ta zauna gidan wani Alhaji Salmanu, wanda mai aje mata masu zaman kan su ne a nan unguwar su, wato Agege. Wata rana aka gayyaci matan gidan Alhaji Salmanu zuwa bikin aure a unguwar Shagamu inda za a yi ajo. Lami ta tafi tare da wata aminiyar ta, Hassana 'yar Jos. Suna isa, suka haɗu da Alhaji Mamman Shata shi ma ya je bikin. Da Shata ya ga Lami, sai ya ga ta yi masa, ya faɗa wa Salmanu. Har ya kawo toshi ya yi mata. Da aka je taron ajo, jama'a ta taru; ga alhazawa da riƙaƙƙun matan Legas, ga kuma ƙanana irin su Lami da Hassana, an zazzauna kan kujeru. Amma hankalin Shata yana kan Lami. Bai ma san sunan ta ba, sai da aka sanya kiɗa zai fara waƙa ya nuna ta ya tambayi maroƙi: "Ya sunan waccan yarinyar?" Maroƙi ya zo ya tambaye ta, duk kunya ta rufe ta, ta ce, "Lami". Maroƙi ya garzaya ya ce wa Shata, "Sunan ta Lami". Buɗar bakin da Shata zai yi ya fara waƙa sai aka ji ya ce, "Yarinya Lami Shagamu!" Alhaji Salmanu ya yi wuf ya je ya raɗa masa a kunne, "A'a, ba 'yar Shagamu ba ce. Ita ma gayyatar ta aka yi." Shata ya ce masa, "Ai waƙa ce, ta riga ta tafi!" Ya ci gaba da rera abar sa. A nan ya fara waƙar. Wannan da ake ji, a situdiyo ya yi ta lokacin da ya je rikodin, kuma ita ce ya yaɗu a duniya. Shata ya fito da Lami a duniya, tare da sauya mata suna daga Lami Adamu zuwa Lami Shagamu. A cewar ta, waƙar ta buɗe mata ƙofofi da yawa, domin duk inda ta shiga aka ce, "Ita ce Lami Shagamu wadda Shata ya yi wa waƙa," sai ka ga ana haba-haba da ita. Hajiya Lami ta je garuruwa a yawace-yawacen ta na wancan lokacin. Wata rana a wani gidan mata da ke Funtuwa wanda ake kira Gidan Shata (mallakin mawaƙin) suka haɗu da Alhaji Shata. Ta je suka gaisa, bai gane ta ba sai da ta faɗa masa ko ita wace ce. Ya yi mamaki sosai. Daga Katsina suke ita da wata ƙawar ta, za su wuce Kaduna, suka tsaya domin su gaisa da wata ƙawar su. Sai Shata ya ce allambaram, su tsaya sai sun kwana a garin. Ya kai su gidan shaƙatawar sa da ke bakin madatsar ruwa ta Mairuwa da ke garin Dukke, inda yake kiwon kadoji, ya karrama su. Washegari suka wuce. Daga bisani dai Hajiya Lami ta tuba, ta yi istigfari, ta yi aure har ta haihu. Ta daɗe da mijin ta kafin auren ya mutu a shekarar 2009. Sai ta ci gaba da riƙe 'ya'yan dangi, musamman saboda 'yar da ta haifa ta rasu. Haka kuma tana 'yan saide-saide tare da haɗawa da siyasa. Lokacin da na yi hira da ita a gidan ta da ke Rijiyar Lemo, Kano, cikin Satumba 2013, tana daga cikin matan ƙungiyar Kwankwasiyya. A da, mukan ɗan yi waya mu gaisa, amma an daɗe ban san halin da take ciki ba. Wannan waƙa da Shata ya yi mata, ta yi daɗi kuma ta yi fice. Kusan kowa na son waƙar. Bayan jigon kambamawa, waƙar tana ɗauke da nasiha kan a daina ƙabilanci ko rikicin addini. Haka kuma Shata ya yi kira ga Musulmi da su haɗa kai, su daina kafirta juna. A waƙar kuma mun ɗan tsinci wani abu game da duniyanci irin na wancan zamanin. Bugu da ƙari, Shata ya fito da unguwar Shagamu a waƙar, fiye ma da yadda ya fito da Agege a waƙar 'Alhaji Na'Allah Ɗan Ibrahim," waƙar da ya yi wa babban ubangidan sa ɗin nan mai cinikin goro a Legas. Abin sha'awa, a gidan Alhaji Na'Allah ɗin ne Lami Shagamu da gwaggon ta ɗin nan suke zaune a wancan lokaci, kuma an sha ɗora wa Lami abinci ta kai wa Shata idan ya sauka a Gidan Baƙi, mallakin Alhaji Na'Allah, idan ya je Legas. A lokacin, tana ƙarama; shi ko ita ba sun cewa hanyoyin su za su gitta da juna har ya yi mata waƙa ba. In ban da Hajiya Lami (ban san halin da take ciki ba), duk waɗanda aka ambata a wannan tsokacin sun riga mu gidan gaskiya. Allah ya jiƙan magabatan mu, ya kyautata namu ƙarshen, amin.